A Nigeria an samu nasarar shawo kan gobarar da ta tashi a kasuwar kantin kwari dake jahar Kano a arewacin kasar. Kungiyar Red Cross ta ce mutane biyu ne suka rasa rayikansu.
Bayan an shafe tsawon lokaci ana ta jayayya yanzu haka an cimma matsaya akan yadda za'a biya diyya ga wadanda harin da kaiwa cibiyar kasuwanci ta birnin New York ya shafa.
Rundunar sojan Najeriya ta karyata zarge-zargen da jami'an gwamnatin jahar Plateau suka yi, cewa ta yi biris da gargadin da aka yi na shirin kai hari wasu kauyuka.
A Nigeria, kungiyar Miyatti Allah ta bayyana takaicinta dangane da abin da ta kira, shafawa Fulani kashin kaji a kan hare-haren baya-bayan nan a jihar Filato.
A Nijar kungiyar 'yan kasuwa na Yamai ta dau matakin rage farashin kayan abinci, a matsayin gudunmawa ga shirin gwamnati na samar da cimaka ga masu fuskantar yunwa.
Duk da cewa dai hukumar kula da muhalli a Abuja ta tsara yadda jama'a za su rika fito da shara, da kuma kwashe ta domin tsaftace birnin, har yanzu shara na ci gaba da dabaibaye manyan titunan birnin.
Rudunar 'yan sadan Jihar Filato ta ce za ta gurfanar da mutane arba'in da tara ne a gaban kotun, da tuhumar su da kisa a rikicin da ya barke kwana kwana nan a rikicin Jos.
Sabon rikici ya sake barkewa a Dogo Nahawa, 'yan kilomitoci kadan daga cikin garin Jos da ke jihar Filato a ranar Lahadi 7 Maris 2010, bayan rikicin watan Janairu.
Hukumar yaki da masu yiwa tattalin arzikin kasa zagwon kasa, wato EFFC ta gurfanar da tsohon gwamnan jihar Nasarawa, Alhaji Abdullahi Adamu a babbar kotun tarraya da ke Lafia babban birnin jihar Nasarawa a ranar Laraba 3 ga watan Maris.
A cikin wata Maris din shekarar 2009 ne Sashen Hausa na BBC ya gudanar da wani rangadi a jihohi goma sha daya na arewacin Najeriya. Rangadin ya mayar da hankali ne kan yadda rayuwa take a yankunan karkara.