A Jamhuriyar Nijar, Jihar Agadez jiha ce wacce Allah Ya huwace mata arzikin ma'adinai da suka hada da Uranium, wanda ake hako shi a kewayen garin Arlit.
Ministocin kudi na kasashe ashirin masu karfin tattalin arziki na taro a Scotland don tattauna batun farfadowa daga matsalar tattalin arziki da kuma kudin magance sauyin yanayi.
Yayinda ake tunkarar zabubbukan shekarar 2011 a Najeriya, 'yan siyasa a Jihar Gombe na zargin gwamnatin jihar da musgunawa 'yan adawa ta hanyar amfani da karfin gwamnati.
Shugaba Obama ya yi kira ga jama'ar Amurka da ka da su yi saurin yanke hukunci game da aniyar wani Manjo na soja da ya bude wuta a wani barikin soji da ke jihar Texas ranar Alhamis.
Kungiyar kasashen dake yammacin Afrika ta Ecowas ta ce, dakatarwar da ta yiwa jamhuriyar Niger ba ta da nasaba da abunda ke faruwa yanzu haka a iyakokin Nigeriya da Niger.
A wani mataki na bukukuwan faduwar bango Berlin, matasan Falasdinawa a Gabar Yamma ta Kogin Jordan sun kada wani sashe na bangon da Isra'ila ta gina da ya raba Isra'ilawa da Falasdinawa.
Ministoci da jamian tsaro na kungiyar kasashen yammacin Afrika, watau ECOWAS ko CEDEAO, na wani taro domin samar da hanyar inganta tsaro a kan iyakokinsu .
Aston villa ce zata karbi bakoncin Bolton, a yayinda kuma Portsmouth zata garzaya gidan Blackburn domin su kece raini. Manchester City kuwa zata kare ne da Burnley, sai kuma Tottenham da zata kara da Sunderland. Wolverhampton dai zata karbi bakoncin Arsenal ne.
Nigeriya ta lallas New Zealanda a wasan zagaye na biyu a gasar cin kofin kwallon kafa ta matasa 'yan kasa da shekaru goma sha bakwai da aka buga a Abuja.
Shugaban Kungiyar kwallon kafa ta Chelsea, Ron Gourlay ya ce kungiyar ta na duba yiwuwar, sayarda sunan filin wasanta na Stamford Bridge ga wani kamfani.
Columbia dai ce zata fafata da Turkiya a wasan quarter finals a gasar cin kofin kwallo ta duniya ta matasa 'yan kasa da shekaru goma sha bakwai da Najeriya ke karban bakonci.
Wasu direbobin manyan motoci sun harzuka ranar Alhamis 29 ga watan Oktoba, suka kuma toshe hanyar Enugu zuwa Anaca, sakamakon zargin da suka yi cewa jami'an tsaro na tilasta musu bayar da cin hanci kafin su wuce.
A cikin wata Maris din shekarar 2009 ne Sashen Hausa na BBC ya gudanar da wani rangadi a jihohi goma sha daya na arewacin Najeriya. Rangadin ya mayar da hankali ne kan yadda rayuwa take a yankunan karkara.