'Yansanda a Jamus sunce suna binciken wasannin kwallon kafa kusan dari biyu a Turai da aka yi magudin sakamakonsu. Wani Jami'in hukumar kula da wasan UEFA yace lamarin abin kunya ne.
Kungiyar Tarayyar Turai ta nada shugabanta na farko da ba na karba-karba ba, bisa yarjejeniyar birnin Lisbon. Ana dai ci gaba da tsokaci kan wanda aka nada da ba'a san shi ba sosai a siyasar duniya.
A Najeriya, mata masu juna biyu da dama ne ke rasuwa a wajan haihuwa. Kididdiga ta baya-bayan nan ta nuna cewa mata dubu biyu ne ke rasuwa a cikin dubu dari a wajen haihuwar a arewacin kasar.
Kasar Masra ta umurci jakadanta da ke Algeria da ya komo gida domin tattaunawa tare da shi, a wani mataki da ke nuna yadda dangantaka tsakanin kasashen biyu ta ke kara tabarbarewa.
A Najeriya, gwamnatin kasar ta mayar da martani a kan alkaluman da kungiyar Transparncy International, mai sa ido a kan cin hanci ta fitar, cewa cin hanci ya karu a Najeriyar.
Shugaban Amirka, Barack Obama, ya ce shirin Isra'ila na gina daruruwan sabbin gidaje domin Yahudawa 'yan kama-wuri-zauna, a filayen Falasdinawa da ke gabashin birnin Kudus.
Kocin Manchester United zai fito filin wasa a karawar da Manchester za ta yi da Everton a filinta na Oltraford duk da hukuncin dakatarwar da aka yi masa.
Wasu direbobin manyan motoci sun harzuka ranar Alhamis 29 ga watan Oktoba, suka kuma toshe hanyar Enugu zuwa Anaca, sakamakon zargin da suka yi cewa jami'an tsaro na tilasta musu bayar da cin hanci kafin su wuce.
A cikin wata Maris din shekarar 2009 ne Sashen Hausa na BBC ya gudanar da wani rangadi a jihohi goma sha daya na arewacin Najeriya. Rangadin ya mayar da hankali ne kan yadda rayuwa take a yankunan karkara.