A Najeriya, gwamnatin kasar ta mayar da martani a kan alkaluman da kungiyar Transparncy International, mai sa ido a kan cin hanci ta fitar, cewa cin hanci ya karu a Najeriyar.
Kasar Masra ta umurci jakadanta da ke Algeria da ya komo gida domin tattaunawa tare da shi, a wani mataki da ke nuna yadda dangantaka tsakanin kasashen biyu ta ke kara tabarbarewa.
Kocin Manchester United zai fito filin wasa a karawar da Manchester za ta yi da Everton a filinta na Oltraford duk da hukuncin dakatarwar da aka yi masa.
Wasu direbobin manyan motoci sun harzuka ranar Alhamis 29 ga watan Oktoba, suka kuma toshe hanyar Enugu zuwa Anaca, sakamakon zargin da suka yi cewa jami'an tsaro na tilasta musu bayar da cin hanci kafin su wuce.
A cikin wata Maris din shekarar 2009 ne Sashen Hausa na BBC ya gudanar da wani rangadi a jihohi goma sha daya na arewacin Najeriya. Rangadin ya mayar da hankali ne kan yadda rayuwa take a yankunan karkara.