Gwamnatin Najeriya ta bukaci jakadanta na Libiya ya koma gida, a wani mataki na nuna bacin ranta da wasu kalaman da Shugaba Libiyar, Mu'ammar Gaddafi yayi a kwanan nan.
Kwamitin majalisar dattawan Najeriya kan gyaran fuska ga tsarin mulkin kasar, wadanda suka shafi dokokin zabe, ya mika rahotonsa na farko ga majalisar dattawan kasar.
Jami'an Isra'ila sun ce, wani ma'aikacin gona dan kasar Thailand ya rasa ransa, lokacin da aka harba wani roka, hadin gida, daga yankin zirin Gaza, zuwa kudancin Isra'ilan.
Hukumomi a jihar Pilato sun ce, an kama mutum bakwai da ake zargi da hannu a harin da ya kai ga hallaka mutane goma sha uku, a wasu kayuka na karamar hukumar Riyom.
Shugaba Obama ya kara kaimi, na yunkurin samun goyonbaya ga manufarsa ta dokar gyaran fuska ga harkokin lafiyar kasar, inda ya yi hira da gidan talabijin na Fox News.
Mahukunta a Uganda sun ce suna gudanar da bincike kan musababbin rasuwar mutane ukku wadanda jamian tsaro suka bindige har lahira, bayan wata gobara da ta lakume wata makabartan sarauta mai tarihi.
Hukumomi a Ghana na ta kokarin hana barkewar wani sabon rikici tsakanin kabilun Ashanti da na Brong Ahafo, a yayin da bangarorin biyu suke jan damarar yaki
Majalissar dokokin Nigeria ta ce zata fito da sabuwar dokar zabe. Hakan ya biyo bayan fitar da jaddawalin zabe biyu da hukumar zaben kasar mai zaman kanta ta yi.
Wasu bama-bamai guda biyu sun tashi a gidan gwamnatin jihar Delta da ke Warri gab da za a fara wani taron neman zaman lafiya. Kungiyar MEND ta bayyana cewa ita ce ke da alhakin dasa bama baman.
Duk da cewa dai hukumar kula da muhalli a Abuja ta tsara yadda jama'a za su rika fito da shara, da kuma kwashe ta domin tsaftace birnin, har yanzu shara na ci gaba da dabaibaye manyan titunan birnin.
A Nijeriya, wata gobara da ta tashi a kasuwar kantin kwari dake jahar Kano a arewacin kasar, ta yi sanadiyyar konewar dubban shaguna da kuma asarar kaya na biliyoyin Nairori.
A cikin wata Maris din shekarar 2009 ne Sashen Hausa na BBC ya gudanar da wani rangadi a jihohi goma sha daya na arewacin Najeriya. Rangadin ya mayar da hankali ne kan yadda rayuwa take a yankunan karkara.